Close Menu
  • Home
  • News
  • Bollywood
  • Entertainment
  • General sports
    • Basketball
    • Boxing
    • Football
    • Hand ball
    • Race
  • Kannywood
  • Traditional sports
    • Dambe
    • Kokowa
    • Langa
    • Shadi
  • HAUSA
    • Labarai
    • Labari
Latest Posts

Ahmed Ololade, known globally as Asake,

July 6, 2026

Prominent Nigerians who founded the PDP party in 1998.”

July 4, 2026

Kannywood stories

July 4, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram
Facebook X (Twitter) Instagram
PULSE SPORTS ENTERTAINMENTPULSE SPORTS ENTERTAINMENT
Advertise With Us
  • Home
  • News

    Prominent Nigerians who founded the PDP party in 1998.”

    July 4, 2026

    The first states in Nigeria were created on May 27, 1967, by General Yakubu Gowon (then Head of State). Before that,

    January 31, 2026

    The major states in Nigeria with known antimony deposits or occurrences include:

    January 26, 2026

    Nigeria has several states where diamond deposits have been reported or identified, though diamond mining is not

    January 25, 2026

    Nigeria has gold deposits in several states, primarily in schist belts across the country. Gold is found in both northern and southwestern regions, with artisanal and small-scale mining common in many areas.

    January 25, 2026
  • Bollywood

    Love luxury, traveling and blogging? Have a huge Instagram following? Expert at creating amazing

    December 7, 2025

    Manoj Bajpayee brought the whole team together for a fun and relaxed Family Man Season 3

    December 6, 2025

    Cikin Dukiyar da Jarumi Dharmendra da ya bari crores 450 an tabbatar da crores 5 baza ta tafi zuwa ga yaran sa ba domin akwai wani family a Punjabi da za a bawa.

    December 3, 2025

    Maganar da Jarumi Sunil shetty ya fada kwanan nan akan yan South India sun fi so su bawa yan Bollywood dama su fito a mugu shiyasa yadaina

    November 29, 2025

    AMITABH yana karanta Alkur’ani. Shekarun baya Amitabh ya fito ya bayyanawa duniya cewa yana karanta Alkur’ani mai girma domin samun nutsuwa tare da kwanciyar hankali.

    November 29, 2025
  • Entertainment

    Ahmed Ololade, known globally as Asake,

    July 6, 2026

    Kannywood stories

    July 4, 2026

    Kannywood Actress

    July 3, 2026

    Dragons of martial arts cinema Donnie Yen, Jackie Chan, Jet Li, and Bruce Lee.

    December 28, 2025

    Happy 31st Birthday to Pretty Jyoti Amge🎉🎂🍰

    December 23, 2025
  • General sports
    1. Basketball
    2. Boxing
    3. Football
    4. Hand ball
    5. Race
    6. View All

    🚨🏴󠁧󠁢󠁥󠁮󠁧󠁿 Barcelona made progress in talks over personal terms with Marcus Rashford

    February 28, 2026

    👕🎁 Paolo Maldini has sent his own match worn shirt from back in the days

    February 28, 2026

    lokutan da za a ɓarje gumi tun daga zagayen ƴan 16 har zuwa wasan ƙarshe: ✅🏆

    February 27, 2026

    January 22, 2026

    “Seeing ourselves up there creates excitement, generates a great atmosphere, and is something to be proud of.”

    November 12, 2025

    A decree from Pope Leo’s office firmly rejects the claim that Mary, Jesus’ mother…

    November 8, 2025

    🚨🏴󠁧󠁢󠁥󠁮󠁧󠁿 Barcelona made progress in talks over personal terms with Marcus Rashford

    February 28, 2026

    👕🎁 Paolo Maldini has sent his own match worn shirt from back in the days

    February 28, 2026

    lokutan da za a ɓarje gumi tun daga zagayen ƴan 16 har zuwa wasan ƙarshe: ✅🏆

    February 27, 2026

    January 22, 2026
  • Kannywood

    Kannywood stories

    July 3, 2026

    Kannywood stories

    July 3, 2026

    Wane ne sabon sufetan ƴansandan Najeriya Tunji Disu?

    February 25, 2026

    G-Fresh Na Shirin Dawo Da Tsohuwar Matarsa Maryam, Bayan Jita-

    January 13, 2026

    Raham Saidu ta gamu da Zolayan Masu bibiyarta kan Bidiyon da ta Saka a

    January 8, 2026
  • Traditional sports
    1. Dambe
    2. Kokowa
    3. Langa
    4. Shadi
    5. View All

    Barcelona player

    November 8, 2025

    Barcelona player

    November 8, 2025
  • HAUSA
    1. Labarai
    2. Labari
    3. View All

    KUNDIN AIKIN JARIDA 2

    July 3, 2026

    Wannan Hoton Wani Babban Mutum Ne Da Iyalinsa a Lokacin Samartaka, Sananne Ne A

    January 4, 2026

    BAZAN GUDU IN BAR AL’UMMATABA IN JI SARDAUNAN SOKOTO.

    December 18, 2025

    JIHAR DA TAFI KOWACE JIHA YAWAN MUTANE A NAJERIYA 🔥 

    December 12, 2025

    Yadda kan iyakar Najeriya da Nijar da Benin ta zama cibiyar ƴanbindiga’

    February 28, 2026

    Ko za a iya dakatar da Shari’ar Musulunci a Arewacin Najeriya?

    February 25, 2026

    🔥 kudin da ya fi rashin daraja (mafi rauni ko mafi ƙarancin ƙima a duniya) a yanzu shine Lebanese Pound (LBP) na Lebanon.

    January 30, 2026

    Gwamnatin Amurka ta mika muhimman kayayyakin soji ga Najeriya domin tallafa wa ƙoƙarin da take yi na yaki da

    January 13, 2026

    KUNDIN AIKIN JARIDA 2

    July 3, 2026

    Yadda kan iyakar Najeriya da Nijar da Benin ta zama cibiyar ƴanbindiga’

    February 28, 2026

    Ko za a iya dakatar da Shari’ar Musulunci a Arewacin Najeriya?

    February 25, 2026

    🔥 kudin da ya fi rashin daraja (mafi rauni ko mafi ƙarancin ƙima a duniya) a yanzu shine Lebanese Pound (LBP) na Lebanon.

    January 30, 2026
PULSE SPORTS ENTERTAINMENTPULSE SPORTS ENTERTAINMENT
Home » KUNDIN AIKIN JARIDA 2
Labarai

KUNDIN AIKIN JARIDA 2

Yusif Saraki MadigawaBy Yusif Saraki MadigawaJuly 3, 2026
InShot 20260703 084931826

KUNDIN AIKIN JARIDA (2)

12 GA YUNI: LOKACIN DA NAJERIYA TA SHIGA MUMMUNAN RIKICI

Rahotannin da muka bayar a BBC bayan soke zaben shugaban kasa na ranar 12 ga Yunin 1993, sun nuna yadda Najeriya ta fada cikin daya daga cikin mafi munin rikice-rikicen siyasa tun bayan samun ’yancin kai. A kankanin lokaci, yanayin kasar ya fara sauyawa.

Tambayar da aka dinga yi a ciki da wajen Najeriya ita ce: “Ta yaya za a soke zaben da aka riga aka gudanar?”

Kafin ka ce kwabo, mamaki ya rikide, jama’a suka fusata. Mun ta ba da rahotannin yadda dubban mutane suke fita kan tituna suna zanga-zanga domin nuna rashin amincewarsu. Kungiyoyin fararen hula, dalibai, kungiyoyin kwadago, masu fafutukar dimokradiyya, lauyoyi, ’yan jarida da talakawa, duk suka yi Allah wadai da soke zaben.

A yanzu da nake karanta kundi na, sai na karanto cewa wancan fushin ya hada mutanen Najeriya ba tare da la’akari da bambancin kabila ko addini ba.

Ba shakka, Najeriya ta fada cikin rudani da rashin tabbas. Babu wanda ya san abin da zai biyo baya. A shirye-shiryen BBC Hausa, mun ta yin sharhi tare da yin tambayoyi kamar: Shin sojoji za su janye soke zaben? Shin za a sake gudanar da wani zabe? Shin za a ayyana Abiola a matsayin shugaban kasa? Ko kuwa Janar Ibrahim Babangida zai ci gaba da mulki har sai illa masha Allahu? Kusan kowace rana akan tashi da wata sanarwa ko kuma jita-jita.

Ana cikin haka, zanga-zanga ta barke a sassa daban-daban na kasar, musamman a Kudu maso Yamma. Mun ta ba da rahotanni kan manyan tarurrukan nuna adawa, yajin aiki, laccoci, zanga-zangar dalibai da kuma matakan da kungiyoyin kwadago suka dauka.

Jama’a kuwa suka ci gaba da bijirewa. A wasu birane an rufe hanyoyi da kasuwanni, yayin da wasu kamfanoni suka dakatar da ayyukansu. A hankali, harkar tafiyar da Najeriya ta fara sarkakewa.

Kwatsam sai aka fara kama mutane, ana tsare su ba tare da an yi musu shari’a ba. Mun yi labaran kama masu rajin dimokradiyya, shugabannin kwadago, shugabannin dalibai, ’yan siyasa da ma ’yan jarida. Mu kuwa, duk da cewa muna London, mun kwana da sanin cewa a kowane lokaci ana iya gayyatar masu aiko mana da rahotannin da ke zaune a Najeriya.

A gare ni da kaina, wannan lokaci ya zama wani babban juyin juya hali a rayuwata ta aikin jarida. BBC ta zama daya daga cikin manyan kafafen da ’yan Najeriya suka dogara da su wajen bibiyar abubuwan da ke faruwa. Duk wata sanarwa daga Abuja kusan nan take muke ba da rahotonta. Haka ma duk wani martani daga gwamnatocin Birtaniya da Amurka, kungiyar Commonwealth da sauran kasashen duniya. Sannu na fara kallon kai na a matsayin wata wadda ke da wani babban nauyi akai na.

Matsin lamba ya ci gaba da karuwa. Bayan makonni ana zanga-zanga tare da matsanancin suka daga kasashen waje, sai Janar Babangida ya sanar a ranar 26 ga Agustan 1993 cewa zai “koma gefe” (stepping aside).

Amma maimakon ya mika mulki ga wanda mutane da dama suka dauka shi ya lashe zaben, wato Chief Abiola, sai ya kafa Gwamnatin Rikon Kwarya karkashin jagorancin Chief Ernest Shonekan.

Sai dai ’yan Najeriya kalilan ne suka yi imanin cewa rikicin siyasar Najeriya ya kare a nan.

#jamilahtangaza #June12 #nigeriademocracy

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X
Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram LinkedIn Email
Yusif Saraki Madigawa
  • Website
  • Facebook
  • X (Twitter)
  • Instagram

Related Posts

Wannan Hoton Wani Babban Mutum Ne Da Iyalinsa a Lokacin Samartaka, Sananne Ne A

January 4, 2026

BAZAN GUDU IN BAR AL’UMMATABA IN JI SARDAUNAN SOKOTO.

December 18, 2025

JIHAR DA TAFI KOWACE JIHA YAWAN MUTANE A NAJERIYA 🔥 

December 12, 2025

Muntina da Aisha Bello Mustapha ‘ yau 11 December shine watan data koma ga Allah ‘ take cika shekara 2 da rasuwa 11/12/2023 -11/12/2025

December 11, 2025
Add A Comment

Leave a ReplyCancel reply

Latest Posts
Advertisement
© 2026 PULSE SPORTS ENTERTAINMENT. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Disclaimer
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.